Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Palstine info cewa; Ministan harkokin wajen kasar Sweden ya ki amincewa ya gana da ministan harkokin wajen Haramtacciyar kasar Isra'ila Liberman. Ministan na kasar Sweden ya ki amincewa ya gana da ministan harkokin haramtacciyar gwamnatin yahudawan ne sakamakon sace bangarorin jikin palastinawa da suka kashe ne suna sayarwa kasashen yammacin turai, wanda gwamnatin Sweden take kallon hakan a matsayin wani mummunan aiki. 469669