Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce ta watsa rahoton cewa; ta nakalto daga majiyar fadar shugaban kasar Iran Ahmadi najad cewa lokacin ganawarsa da babban sakataren majalisar dinkin duniya sun tabo halin da palasdinawa ke ciki a yau da kumcin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ta sanya su a ciki tare da tunanin hanyoyin kawo karshen halin da suke ciki da kuma yankin gabas ta tsakiya baki daya. Wannan ganawa dai ta z one a daidai lokacin gudanar da babban taron majalisar dinkin duniya da aka gudanar a birnin Newyork na kasar Amerika.
469810