Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani bayani da ya nakalto daga shafin yanar gizo na kungiyar raya al'adu da ilmi a kasashen musulmi ta ISESCO, inda bangaren yada labaran kungiyar ya habarta cewa, an gabatar da wata kujera da aka yi da haruffan larabci, bayan da aka sassaka su a matsayin bangarorin kujerar a jami'ar Niger da ke birnin Yamai fadar mulkin kasar. Bayanin ya ci gaba da cewa babbar manufar gabatar da wannan kujera shi ne kiyaye yaren addini, tare da saka shi a matsayin daya daga cikin abubuwa na tarihi a kasar. 565670