Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, kamfanin dillancin labaran kur'ani na muzn ya habarta cewa, an bude wata cibiya ta koyar da yara 'yan makaranta karatun kur'ani mai tsarki da ilmomin fikihu da akidar musulunci a birnin Karbala mai alfarma na kasar Iraki. Bayanin ya ci gaba da cewa wannan shiri bayar da horo zai kebanci kanan yara ne, zai kasance a matakan firamare da sakandare. An bude wannan bangare ne a cikin hubbaren Imam Hussain (AS) da ke cikin birnin mai alfarma.602439