IQNA

An Ayyana Wakilin Birtaniya A Kungiyar Kasashen Musulmi

19:36 - June 27, 2010
Lambar Labari: 1946898
Bangaren kasa da kasa; Bayan da kasashen Rasha da Amurka Birtaniya ma ta tura nata wakiliyarta a kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jaridar zaman ta kasar Turkiya ta habarta cewa, bayan da kasashen Rasha da Amurka suka tura wakilansu a kungiyar kasashen musulmi ta OIC gwamnatin Birtaniya ma ta tura nata wakilin da zai wakilce ta a cikin kungiyar. Bayanin ya ci gaba da cewa musulma ta farko a cikin majalisar ministocin fira ministan kasar Birtaniya Kate Rodd, ita ce wakiliyar kasar a kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC, inda za ta ci gaba da wakiltar kasar a dukkanin tarukan da kungiyar take gudanarwa. 604088



captcha