Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran Ikna daga reshenta a kasar Jodan ta watsa rahoton cewa; shugaban da ke kula da harkokin addini a lardin Ukba na Jodan ya bada labarin bude tsangayar hardar kur'ani a Masallatai guda dari da arba'in da hudu. Sheikh Suleiman Balil ya kara da cewa; burin wannan tsangayar karatun Kur'ani da bude wadannan cibiyoyi shi ne karfafawa matasa karfin guiwar rungumar karatun kur'ani da bawa wannnan bangare mai muhimmanci matsayinsa na hakika a rayuwa da addini.
604564