Bangaren kasa da kasa; A yau lahadi za a fara gudanar da kasuwar baje kolin littafan kasar Iran a birnin Karbala mai alfarma, wanda cibiyar bunkasa harkokin ilmi da ala'adu ta jamhuriyar musulunci ta dauki nauyin shiryawa da gudanarwa.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari day a nakalto daga bangaren hulda da jama'a na cibiyar kula da bunnakasa harkokin al'adu da ilimi cewa, a yau lahadi za a fara gudanar da kasuwar baje kolin littafan kasar Iran a birnin Karbala mai alfarma, wanda cibiyar bunkasa harkokin ilmi da ala'adu ta jamhuriyar musulunci ta dauki nauyin shiryawa da gudanarwa a birnin mai alfarma.
Bayanin ya ci gaba da cewa wannan dai ba shi ne karon farko da ake gudanar da irin kasuwar baje koli ta madaba'antun kasar Iran a kasar Iraki ba, amma a wannan karon baje kolin zai samu halartar cibiyoyin buga littafai da dama.
623861