Bangaren kasa da kasa; Za a gudanar da silsilar zaman sauraren karatun kur'ani mai tsarki a birnin London fadar mulkin kasar Birtaniya, wanda za a gudanar a cikin watan Ramadan mai alfarma tare da halartar makaranta kur'ani daga sassa daban-daban na kasar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na ic-el an habarta cewa, za a gudanar da silsilar zaman sauraren karatun kur'ani mai tsarki a birnin London fadar mulkin kasar Birtaniya, wanda za a gudanar a cikin watan Ramadan mai alfarma tare da halartar makaranta kur'ani daga sassa daban-daban na kasar ta Birtaniya.
Bayanin ya ci gaba da cewa, za a gudanar da zaman sauraren karatun kur'ani a kowace rana kafin sallolin magriba da isha'i a cikin watan mai alfarma.
Shugaban cibiyar kula da harkokin muslunci ta birnin London Mohammad said Bahmanpour shi ne zai jagoranci gudanar da zaman sauraren karatun kur'anin.
627821