IQNA

Jami'ar Al-Mostafa (SAW) Na Da Shirin Gina Wasu Cibiyoyin Ilimi

13:05 - August 26, 2010
Lambar Labari: 1981699
Bangaren kasa da kasa; Jami'ar Al-mostafa (SAW) tana hanyoyi da daman a bunkasa harkokin ilmi a cikin kasashen musulmi, kuma ahalin yanzu akwai karanci cibiyoyin addinin Musulunci a cikin wasu kasashen musamman ma wadanda ban a musulmi ba.


Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, sheikh Kasim shugaban cibiyar rasul a'azam a kasar Thailand ya bayyana cewa, jami'ar Al-mostafa (SAW) tana hanyoyi da daman a bunkasa harkokin ilmi a cikin kasashen musulmi, kuma ahalin yanzu akwai karanci cibiyoyin addinin Musulunci a cikin wasu kasashen musamman ma wadanda ba na musulmi ba ke cikin nahiyar Asia.

Malamin ya ci gaba da cewa ya kamata jami'ar Al-mostafa (SAW) ta kara maida himma wajen bude wasu cibiyoyin a cikin irin wadannan kasashe sakamakon karancin wuraren gudanar da harkokin addinin Musulunci, tare da bunkasa cibiyoyin da ke akwai a halin yanzu.

A bangare guda ya yaba da irin rawar da wannan jami'a take takawa wajen habbaka harkokin ilmin addinin Musulunci a cikin gida da kuma kasashen ketare.

640715






captcha