Bangaren kasa da kasa, kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ta jaddada wajabcin kai taimako zuwa ga al’ummar kasar Libya da ke fuskantar kama karya daga Mu’ammar Gaddafi, inda yanzu haka dubban daruruwan mutanen kasar suke cikin mawuyacin hali.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na OIC an bayyana cewa, kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ta jaddada wajabcin kai taimako zuwa ga al’ummar kasar Libya da ke fuskantar kama karya daga Mu’ammar Gaddafi, inda yanzu haka dubban daruruwan mutanen kasar suke cikin mawuyacin hali na firgici da kuma barin muhallanasu.
A wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Nasij an bayyana cewa, za aguudanar da wani zaman taro na kara wa juna sani kan mu’ujizar ilimin kur’ani mia tsarki da kuma sunnar manzon Allah (SAW) wanda za agudanar a karo na goma a birnin Istanbul fadar mulkin kasar Turkiya, tare da halartar masana daga sassa na kasashen duniya, musamman ma daga kasashen larabawa da na musulmi.
Bayanin ya ci gaba da cewa wannan zaman taro an sabar gudanar da shi a kasar ta Turkiya, wanda ma’aikatar kula da ayyukan addinin musuluci ta kasar ta kan dauki nauyin shiryawa da gudanarwa a kowace shekara, tun daga shekara ta dubu biyu da daya da ta gabata, inda masana kan gabatar da laccoci da kuma makalolin da suka tanada kan hakan.
762737