IQNA

An Buga Tare Da Yada Littafin Nan Mai Suna Raya Tunanin Addinin Muslunci

19:46 - April 30, 2011
Lambar Labari: 2114721
Bangaren kasa da kasa, an buga tare da yada littafin nan mai suna raya fikirar addinin muslunci da hanyoyin isar da ita ga sauran al’ummomin duniya, wanda aka rubuta a cikin harshen larabci kuma aka tarjama shi zuwa wasu manyan yaruka na duniya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo an bayyana cewa an buga tare da yada littafin nan mai suna raya fikirar addinin muslunci da hanyoyin isar da ita ga sauran al’ummomin duniya, wanda aka rubuta a cikin harshen larabci kuma aka tarjama shi zuwa wasu manyan yaruka na duniya, wanda cibiyar yada ayyukan ilimi da al’adun musulunci ta ISESCO ta daukinauyin bugawa.
A wani labari da ya nakalto daga shafin sadrawa na yanar gizo na algeriesoir an bayyana cewa, an gudanar da sallar juma’a abirnin Rom fadar mulkin kasar Italia a babban dandalin da ke tsakiyar birnin, domin nuna rashin amincewa da matakin da mahukuntan suka dauka na kin bayar da izinin gina masallaci a birnin wanda ake kallaonsa amatsayin babban birnin na mabiya addinin kirista.
Bayanin ya ci gaba da cewa mabiya addnin muslunci na kasar Italia musamman ma mazauna birnin Rom, suna ganin cewa bisa la’akari da yawan da suke da shi a kasar, daidai da ddokokin da aka amince da su auna da ahakkin su mallaki babban masallacin juma’a a cikin birnin Roma, kuma sun aike da takardun neman izini kan hakan, amma har yanzu mahukunta ba su ce komai ba.
782938
captcha