Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa ya naklato daga shafin sadarwa na aynar gioz na FNC cewa an fara gudanar da wani zaman taro na majalisun dokoki na kasashen musulmi a birnin Dubai na kasar hadaddiyar daular larabawa wanda ke samun halartar wakilai daga kasashen musulmi da na larabawa daya daga cikin mambobi a kungiyar hadin kan kasashen musulmi.
A wani labarin kuma babban malamin addinin muslunci mai bayar da fatawa akasar Serbia ya tsaya takarar neman kujerar majalisar dokokin kasar a zabukan da za a gudanar a nan gaba da nufin zama mai wakiltar musulmi a majalisar dokin kasar ta Serbia wadda musulmi ne marassa rinjaye a cikinta.
Da dama daga cikin masana musulmi sun imanin cewa abubuwan da suka faru na cin zarafin musulmi da addinin muslunci a kasashen turai, da hakan ya hada da yada hotuna na zanen batunci ga manzon Allah tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da iyalan gidansa tsarkaka, wata alama ce da ke nuni da cewa al’ummomin wadanan kasashen da ‘yan siyasarsu da shugabanninsu suna yin amfani da nuna adawa da musulunci da kuma yada kyamarsa atsakanin mutane a matsayin wata hanya ta neman matsayi na siyasa ko zamantakewa a cikin kasashen da suke gaba da musulmi da musulunci.
Har ila daga cikin irin wadannan munanan ayyukan da irin wadannan mutane suke aiwatarwa a kasashen yammacin turai har da sanar da ranar kone kur’ani ta duniya da wani la’antacen mutum ya yi a kasar Amurka ba tare da an ce masa uffan ba, da kuma zanga-zangar da wasu mutane suka yi akasar Jamus ta gaba da musulunci, daga karshe-karshen nan kuma sojojin Amurka sun banka wuta kan kur’ani mai tsarki a kasar Afghanistan.
1031791