IQNA

Taron Buda Baki Da Ya Hada Musulmi Da Kirista A Garin kaduna Da ke Nigeria

14:35 - July 25, 2012
Lambar Labari: 2377451
Bangaren kasa da kasa, an gudanar da wani taron buda baki wanda ya hada mabiya addinin muslunci da suka yi azumi da kuma mabiya addinin kirista domin kara dankon alaka da zumunci tsakanin bangarorin biyu da suka kwashe tsawon shekaru suna rayuwa tare da juna duk kuwa da matsalolin da ake ta kokarin haddasawa a tsakaninsu.


Kamfanin dilalncin labaran iqna ya ahbarat cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na On Islam, cewa an gudanar da wani taron buda baki wanda ya hada mabiya addinin muslunci da suka yi azumi da kuma mabiya addinin kirista domin kara dankon alaka da zumunci tsakanin bangarorin biyu da suka kwashe tsawon shekaru suna rayuwa tare da juna duk kuwa da matsalolin da ake ta kokarin haddasawa a tsakaninsu wanda kai tsaye ake zargin cewa kasashen ketare da suke tare da yahudawan sahyuniya suna da hannu a ciki.

A wani bangare kuma na siyasar kasar komitin bincike na shugaban tarayyar Nigeria kan almundahanar kudaden tallafin man fetur a kasar ya bayyana cewa kamfanonin yan kasuwa wadanda suke shigo da man fetur daga kasashen waje sun karbi naira biliyon 382 daga asusun gwamnati ba tare da sun shigo da ko digo guda na man fetur ba.
Komitin binciken dai karkashin jagorancin Imokhuede, yana daga cikin jeren komiti komiti wadanda suka gudanar da bincike kan wannan almundahanar, kuma ya tabbatar da cewa jami'an gwamnati da dama suna da hannu a cikinsa, Imokhuede, ya bayyana haka ne a jiya a lokacin da yake mikawa shugaba Good luck Jonathan sakamakon binciken komitin nasa.
Shugaban komitin bai ambaci sunan wani kamfani ba, amma ya ce mataki na gaba shi ne shirin gabatar da wadannan kamfanoni da jami'an gwamnatin da suke da hannu cikin almundahanar da kuma auditoci masu zaman kansu wadanda suka kula da shirin bada kongilar a gaban kotu.
1061260









captcha