
Kamfanin
dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadawa na yanar
gizo na jaridar Qods Alarabi cewa, mahkuntan Masar sun hana a gabatar da
littafan ‘yan kungiyar Ikhwan a baje kolin litatfai na duniya wanda ake
gudanarwa a birnin Alkahira tare da halaratar madaba’antu.
A lokacin da
yake ganawa da wasu daga cikin masu halartar wurin Sharif Ismail firayi
ministan kasar Masar ya bayyana cewa, an dauki mataki tantance masu gabatar da
littafansu a wannan wuri, kuma ba za a bar wasu su kawo littafansu ba.
Ya ce
kungiyar yan uwa musulmi na daga cikin wadanda ba za abari su baje littafansu a wannan wuri ba,
domin kuwa an abukatar littafai ne wadanda za su taimaka wajen samun hadin kai
da zaman lafiya a duniya.
Wannan
mataki dai bai yi wa da dama daga cikin mabiya wannan kungiya dadi ba, domin
kuwa tun tsawon shekaru da kungiyar take shiga wannan baje koli ba a taba hana
baje littafanta ba.
Wasu daga
cikin daliban jami’oi na kasar ta Masar da suka je wurin sun ce wannan abin ban
dariya da kuma kunya ga mahukuntan kasar ta Masar, domin kuwa hana baje
littafan ikhwan ba zai hana su samun karbuwa ba.
Daga karshe
dai an bayyana cewa kungiyar tana a matsayin haramtatta ne, kuma duk wani abu
nata ko da aka dangata da ita ya haramta a hukumancea kasar ta Masar.