
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga
shafin sadarwa na yanar gizo na aqlame.com cewa, a jiya ne aka bude zaman taron
karatun kur'ani mai tsarki mai taken taimakon Allah da manzonsa (SAW) a otel na
Khater a birnin Nuwakshot.
Sheikh Ali Rida bin Muhammad Naj Alsu'aidi shugaban cibiyar kula da
ayyukan kur'ani mai tsarki ta taimakon Allah da Manzo (SAW) shi ne ya jagoranci
bude taron, inda Sayyid Muhammad bin Mahmud bin Badi ya gabatar da jawabi ga
mahalarta taron.
Inda y ace kur'ani yana koyar da dan adam abubuwa da dama da suka
hada da hakuri, gidun duniya, hakuri, godiya, kaunar juna, fata, tsoro, dogaro
da Allah, yarda da Allah da abin da ya kaddara.
Bayanin ya ci gaba da cewa babar manufar gudanar da wannan taron
karatun kur'ani mai tsarki ita ce tunatar da musulmi dangane da koyarwar wannan
littafi mai girma, wanda Allah ya safkar ga manzonsa domin ya zama jagora da
shiriya ga bil adama baki daya.
Bayan karatun kur'ani an gabatar da wakokin yabon manzon Allah
(SAW) a wurin, kamar yadda kuma wasu malaman suka gabatar da jawabai na
fadakarwa ga malarta taron.
Tashar talabijin ta Alhurra ta watsa wannan taro kai tsaye a
lokacin da ake gabatar da shi daga birnin Nowakshot.