Kamfanin dillancin labaran iqna ya
habarta cewa ya nakalto daga shafin yada labarai na Evenin Standard ya bayar da
rahoton cewa, Cliss Wenson kakakin rundunar 'yan sanda na birnin malmo ya sheda
wa manema labarai cewa, suna cikin farautar mutumin da ya kai hari kan wannan
makarata ta musulmi.
Bayanin ya ce bayan da aka cinna wuta kan wannan makaranta, 'yan sanda sun ga
wani mutum a lokacin yana tsrewa daga wurin a cikin wata mota, kuma sun bi shi
amma yaki tsayawa, kuma daga bisani ya tsere musu, duk kuwa da cewa su yi ta
yin harbi da bindiga domin tsayar da shi.
A cikin makonni da suka gabata an kai hare-hare a kan makarantun mabiya addinin
muslunci a garuruwa daban-daban na kasar ta Sweden, da ma wasu cibiyoyin addini
na musulmi, kamar yadda aka kai wasu hare-hare kan sansanonin 'yan guun hijira,
wadanda akasarinsu musulmi ne.