
Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, gasar kur’ani ta Algeriya za a gudanar da ita ne nan da yan kwanaki masu zuwa daga 20 zuwa 26 ga watan Ramadan mai alfarma.
An haifi Muhammad Rasul Takbiri a birnin Tehran, kuma ya kasance yana da tsari na musamman wajen hardar kur’ani mai tsarki.
A shekarar da ta gabata ce dai ya karbi takardun shedar kamala hardar kur’ani mai tsarki, kuma takardunsa sun nunaa cewa hardarsa tana da kyau matuka.
Haka nan kuma a shekarar da ta gabata Muhammad Khakpour wanda ya zo na biyu a gasar kur’ani ta kasa baki shi ne ya wakilci Iran a gasar kur’ani ta kasar Algeriya.
Ali Reza Faizi da Paiman Ayazi, su ne suka wakilci Iran a gasar duniya ta kasar Algeriya a cikin shekarun 2013 da kuma 2014, inda suka samu matsayi na hudu a gasar baki daya.