Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga tashar
talabijin ta Press TV ta bayar da rahoton cewa, jami'an 'yan sandan sun
kaddamar da farmakin ne a kan gidan Abdulrahim Ali Alfaraj, bisa zarginsa da cewa
ya jefi jami'an tsaro, bayan kashe shi har lahira bisa wannan zargi a yammacin
jiya Laraba, jami'an 'yan sanda na masarautar mulkin mulukiyya ta Al Saud sun
rusa gidan baki daya.
Tun a cikin watan Fabrairun shekara ta 2011 ce dai alummar yankunan gabashin kasar saudiyya wadanda mabiya mazhabar shi'a ne, suka fara yunkurin ganin an ba su hakkokinsu da ake danne musu a matsayinsu na 'yan kasa, wadanda suke korafin cewa dukkanin arzikin kasar na man fetur da iskar gas da tattailin arzikin kasar ya dogara akansa, daga yankinsu ake fitar da shi, amma suna rayuwa a cikin yunwa da talauci da rashin ayyukan yi.
Wannan dai shi ne babban dalilin da ya sanya mahukun kasar Saudiyya suka kame Sheik Bakir Nimr suka kashe, saboda nuna goyon bayansa ga masu fafutukar neman hakkokin al'ummomin yankunan gabashin kasar.