IQNA

Amnesty Int. Ta Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Rusa Masallacin Musulmi A Myanmar

23:53 - June 25, 2016
Lambar Labari: 3480551
Bangaren kasa da kasa, Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International ta yi kakkausar suka dangane da farmakin da wasu 'yan addinin Buda suka kai kan wani masallacin musulmi a kasar Myyanmar tare da kone shi.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin yanar gizo na Ina cewa, A cikin bayanin da kungiyar ta fitar, ta bukaci gwamnatin kasar Myanmar da ta gaggauta gudanar da bicike kan wannan lamari, tare da kame dukkanin wadanda suke da hannu da kuma gurfanar da su a gaban kuliya.

Bayanin ya ce abin da musulmi suke fuskanta na cin zarafi da kisa da tsangwama a kasar Myanmar ya wuce iyaka, kuma hakki a kan gwamnatin kasar ta dauki matakin kare rayukan mabiya addinin muslunci a kasar, domin rashin yin hakan zai sanya alamar tambaya a kan matsayin gwamnatin kasar dangane da abin da ake yi ma muuslmi.

A daren Alhamis da ta gabata ce dai wasu masu bin addinin buda da yawansu ya kai kimanin 200 suka kai farmaki kan wani masallaci a yankin Bago na kasar ta Myyanmar, inda suka banka ma masallacin wuta tare da kone shi kurmus, musulmin da ke wurin sun tsere zuwa wani ofishin 'yan sanda da ke kusa domin samun kariya.

Mabiya addinin muslunci 'yan kabilar Rohingya da suke zaune akasar Myyanmar suna fuskantar matsaloli na kyama da cin zarafi da kisa daga masu tsatsauran raayin addinin Buda, wadanda suke kallon musulmin a matsayin baki haure, kuma dole su bar kasar.

3510163

captcha