Kamfanin
dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar
gizo na Shafin watsa labarai na yanar
gizo mallakin kungiyar Hamas ya bayar da sanarwar cewa, kalaman da suka fito
daga bakin Turki Faisal tsohon shugaban hukumar leken asirin kasar Saudiyya a
gaban taron kungiyar MKO a birnin Paris kan kungiyoyin Palastinawa da ke yaki
da zalunci da mamayar Isra'ila babban abin kunya ne.
Bayanin ya ce kungiyar Hamas da sauran kungiyoyin gwagwarmaya dukkaninsu kungiyoyi ne na palastinawa zalla da suke gwagwarmaya domin kare martabar al'ummar musulmi ta Palastinu da wurare masu tsarki da ke fuskantar tozrci da daga yahudawan sahyuniya, amma bayyana su a matsayin 'yan ta'adda masu yi ma wasu aiki da yarima Turki Faisal ya yi, hakan yana matsayin wata babbar hidima ga Isra'ila, kuma hakan takar an bayar da lasisi ne ga Israila kan ta ci gaba da ta'addancinta kan al'ummar Palastinu.
Ita ma a nata a nata bangaren kungiyar Jihadul Islami ta bayyana kalaman na yarima Turki Faisal da cewa alama ce ta kaskanci da wulakanta kai a gaban yahudawan sahyuniya, ta yadda wani babban jami'i a wannan masarauta da larabawa da musulmi suke kallonta da kima, ya buda baki ya kira masu kare kansu daga zaluncin Isra'ila a matsayin 'yan ta'adda.
A cikin 'yan makonnin da suka gabata, ministan harkokin wajen masarautar iyalan gidan Al Saud Adil Jubair ya furta cewa, nan ba da jimawa ba za su kwace makaman da ke hannun kungiyar Hamas da sauran kungiyoyin palastinawa yan gwagwarmaya.