A cikin bayanin nasa ya kara da cewa dole ne mahukuntan Bahrain su kwana da sanin cewa kasar ba mallakinsu b ace, mallakin al’ummar kasar ce baki daya, saboda haka baya halasta gare su su gudanar da tarukan addini da mafi yawan al’ummar kasar suke gudanarwa.
Haka nan kuma ya kirayi masana da kuma masu kare hakkokin yan adama koina cikin fadin duniya da su sake nauyin da kensu na bayyana wa duniya abin da yake faruwa a kasar Bahrain na zaluncin da al’ummar kasar ke fyskanta.
Kamar yadda kuma bayyana cewa za su dauki dukkanin matakan da suka dace domin ganin an gabatar da wannan batua gaban kotun manyan laifuka ta duniya domin hukunta azzalumai daga cikin masu mulkin kama karya kan al’ummar kasar Bahrain.
Daga karshe ya bayyana bin dayake faruwa kan al’ummar wannan kasa da cewa yana daga cikin nauoin zaluncin da duniya take shedawa a cikin wanan karni.