Jami’an tsaron sun dauki wannan matakin ne tun a daren jiya domin hana gdanar da duk wani taro na juyayin Ashura da aka saba gudanarwa a wurin tsawon daruruwan shekaru.
Jami’an tsaron baya ga rufe hanyoyin isa wurin, sun kuma dauki matakin ganin cewa bas u bari an gudanar da irin wadannan taruka ba kamar yadda aka saba saboda dalilan da ba su bayyana ba.
Wannan lamari dai bai zo ma kowa da mamaki ba, idan aka yi la’akari da yadda gwamnatin kama karya ta kasar Masar take yin biyayya ga masarautar da ke daukar nauyinta tare da ba ta kudaden shiga, wadda ke kan gaba wajen kiyayya da mazhabar iyalan gidan manzon Allah a duniya.