IQNA

Gwamnatin Masar Ta Hana Gudanar Da Tarukan muharram

22:24 - October 13, 2016
Lambar Labari: 3480852
Bangaren kasa da kasa, gwamnatin kasar masar ta dauki matakan mabiya mazhabar iyalan gidan amnzon Allah gudanar da tarukan makokin Ashura.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar alalam cewa, jami'an tsaron kasar Masara cikin kayan sarki sun dauki matakan hana gudanar da tarukan Ashura a masallacin Imam Hussain (AS) da ke Alkahira.

Wannan mataki dai ya zo a cikin kwanakin farko na watan muharram a wanda a cikin su mabiya mazhaba iyalan gidan manzo ke gudanar da taruka har zuwa ranar goma ga watan.

A cikin masalalcin Imam Hussain akwai wani bangare da ake cewa nan ne aka bizne kan Imam Hussain (AS) a lokacin da makiya manzon Allah suka kasha shi.

Tun kafin wannan lokacin dai masu dauke da akidar wahabiyanci da kafirta musulmi sun ta kai komo domin ganin an hana mabiya mazhabar shia gudanar da tarukansu da suka saba yi tsawon daruruwan shekaru a wurin.

3537450


captcha