IQNA

Jakadan Isra'ila A Majalisar Dinkin Duniya:

Shugabar UNESCO An Yi Mata Barazanar Kisa

22:52 - October 18, 2016
Lambar Labari: 3480863
Bangaren kasa da kasa, jakadan haramtacciyar kasar Isra'ila a majalisar dinkin duniya ya bayyana Arina Bukowa shugabar hukumar UNESCO an mata barazanar kisa ne kan kudirin da ta dauka.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na WB cewa, tun bayan da hukumar UNESCO ta bayyana goyon bayanta ga al'ummar Palastinu manyan kasashen duniya masu mara ma Isra'ila baya suka nuna kaduwa.

Abin ya faru jiya a majalisar dinkin duniya babban abin kunya ne, inda jakadan haramtcciyar kasar Isra'ila ya mike yana bayyana cewa an yi barazanar kisa ne akan shugabar UNESCO har ta bayyana cewa masallacin aqsa mallakin msuulmi ne.

Hukumar ta gabatar da wani daftrin kudiri da ke nuna cewa masallacin aqsa na msuulmi, kuma an kada kuri'a kan wannan daftarin kudiri, inda kasashe 58 suka kada kuri'a, wasu 24 sun amince, wasu 6 kuma suka amincewa yayin da 26 suka ki kada kuri'a sai kuma wasu da bas u uffan ba.

Wannan ya zama wata babbar nasara ga al'ummar palastinu da kuma musulmi baki daya, wanda ya tabbatar da cewa su ne suke da hakkin kuma su ne ake zalunta a kan idanun duniya.

3538718


captcha