IQNA

Ana Gudanar Da Taron Makon Kur'ani A Kasar Algeria

21:15 - December 27, 2016
Lambar Labari: 3481074
Bangaren kasa da kasa, An bude babban taron makon kur'ani na kasa karo na 18 a birnin Algiers fadar mulkiin kasar Aljeriya, wanda aka saba gudanarwa a kowace shekara.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, kamfanin dillancin labaran kasar Aljeriya ya bayar da rahoton cewa, an bude wannan taro ne a jiya a babban dakin taruka na cibiyar Mudi Zakariya da ke birnin na Algiers, tare da halartar manyan malamai na kasar, da kuma wasu daga cikin jami'an gwamnati da masana, gami da jakadu na kasashen musulmi da ke kasar Aljeriya.

Shugaban kasar ta Aljeriya Abdulazizi Butaflika wanda bai samu halartar bude taron ba, ya aike da wakilinsa kuma babban mai ba shi shawara kan harkokin addini Muhammad Ali Bu Ghazi, wanda ya karanta jawabin shugaban kasar a gaban mahalarta taron.

A cikin bayanin nasa, shugaba Butaflika ya bayyana muhimamncin gudanar da irin wadannan taruka, domin wayar da kan al'umma dangane da muhimamncin koyarwar kur'ani ga musulmi, da kuma yadda kur'ani mai tsarki yake koyar da musulmi yin aiki da hankali a kowane lokaci, da kuma kyawawan dabiu da zaman lafiya tare da sauran al'ummomi.

Ya kara da cewa babbar matsalar da msuulmi suka shiga ciki a halin yanzu ta samo asali ne da rashin yin riko da koyarwar da ke cikin kur'ani mai tsarki, kamar yadda kuma a daya bangaren wasu masu mummuanr akida suke yin amfani da kur'ani wajen aikata ta'addanci, wanda hakan ke bata sunan kur'ani da kuma musuluncin baki daya aidon duniya.

Wannan taro dai zai ci gaba da guda har tsawon mako guda a nan gaba, inda malamai da masana za su ci gaba da gabatar da bayanai da kuam kasidu, wadanda daga bisani za a wallafa su a littafi guda daya.

3557003


captcha