IQNA

22:47 - April 11, 2017
Lambar Labari: 3481396

Vatican Ta Ce paparoma Zai Yi Tafiya Zuwa Masar

Bangaren kasa da kasa, fadar Vatican ta sanar da cewa, duk da hare-haren da aka kai a kan majami’oin mabiya addinin kirista a kasar Masar, tafiyar Paparoma Francis zuwa Masar na nan darama cikin wannan wata.

Vatican Ta Ce paparoma Zai Yi Tafiya Zuwa Masar

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jaridar Al-shuruq ta kasar Masar ta bayar da rahoton cewa, Fadi Francis daya daga cikin mambobin kwamitin tsara tafiye-tafiyen Paparoma a fadar Vatican ya sheda cewa, tafiyar Paparoma zuwa Masar na nan kamar yadda aka tsara.

Fadi Francis ya ce babu gaskiya a cikin rahotannin da wasu kafofin yada labarai suka yada, da ke cewa Paparoma ya dakatar da tafiyarsa zuwa kasar Masar, sakamakon hare-haren ta’addancin da aka kai a kan manyan majami’iun mabiya addinin kirista a kasar.

A ranar 27 ga wannan wata na Afrilu ne dai paparoma Francis zai kai ziyara ta kwanaki biyu a kasar Masar, inda zai gana da shugaban kasar Abdulfattah Sisi, da kuma babban jagoran mabiya addinin kirista na kasar, gami da babban malamin cibiyar Azhar.

3588807


captcha