IQNA

Karamin Yaro Ya Yi Karatun Kur'ani A Gaban Sarkin Morocco

17:56 - July 02, 2017
Lambar Labari: 3481662
Bangaren kasa da kasa, Zubair Algauri wani karamin yaro da Allah ya yi masa baiwa ta karatun kur'ani mai tsarki, ya yi karatu a gaban sarkin Morocco.
Kamfanin dillancin labaran iqn aya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na 24alyaoum cewa, Zubair Algauri dan shekaru 13 da haihuwa ya yi fice wajen karatun kur'ani mai tsarki a mataki na duniya.

Ya gabatar da karatun kur'ani a daren 27 na watan Radan wanda shi ma ake lissafa shi a cikin dararen lailatun Qadr a wajen wasu malamai, karatun ya guda ne a masallacin Hassan na biyu tare da halartar sarki Muhammad na shida.

Karatun ya dauki hankulan dukaknin mutanen da suke a wurin, kasantuwar ya shahra wajen kiyaye kaidoji na tajwidi da karatun kur'ani mai tsarki.

Wannan yaro dai yana aji na biyu ne a hain yanzu makarantar gabada firamare, kuma si ne ya zo na biyu a gasar karatun kur'ani ta duniya a a birnin Dubai a cikin shekara ta 2013.

An haifi Zubair Algauri ne a garin Kazablanka shekaru 13 da suka gabata, kuma ya yi karatun kur'ani a garin tare da taimakon mahaifansa, inda a halin yanzu shi ne yarin da aka zaba a matsayin yaron da ya fi kowa ta fuskar karatun kur'ani a cikin kasashen larabawa, kuma ya samu kyautar sarki Muhammad na shida.


Karamin Yaro Ya Yi Karatun Kur'ani A Gaban Sarkin Morocco


captcha