IQNA

Mahangar Tsohon Mai bayar Da Fatawa Na Masar Kan Kur’ani Lokacin Manzo

23:21 - February 25, 2018
Lambar Labari: 3482427
Mahangar Tsohon Mai bayar Da Fatawa Na Masar Kan Kur’ani Lokacin Manzo
Bangaren kasa da kasa, Ali Juma’a tsohon muftin kasar Masar ya bayyana cewa’anin da ke akwai lokacin manzon Allah yana da nakasu a cikin rubutunsa.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a lokacin da ake zantawa da shi a tashar talabijin ta CBC ta kasar Masar a jiya, Ali Juma’a tsohon muftin kasar Masar ya bayyana cewa’anin da ke akwai lokacin manzon Allah yana da nakasu a cikin rubutunsa da kuma jerin ayoyinsa da surorori.

Ya ce a lokacin manzo kur’ani bas hi da alamu da wasulla da kuma digagga, kamar yadda ayoyinsa da surorinsa a jere suke ba, wanda daga bisani ne aka yi aikin tsara su.

Ya kara da cewa kur’anin da ke akwai lokacin manzo babu sunayen surori a cikinsa a rubuce, ana fadinsu ne kawai da baki amma ba a rubuce ba.

Da dama daga cikin malami masu bincike sun ce an hada ayoyin kur’ani a lokacin manzo, amma bayan rasuwarsa a lokacin halifa na uku ne aka hada kur’anai domin kada a samu banbancin kwafin da ke hannun mutane a biranen musulmi.

3694367

 

 

 

 

captcha