IQNA

Jakadan Vatican Ya Yaba Da Kyautar Da Ya Samu Daga Iran

21:06 - March 01, 2018
Lambar Labari: 3482443
Bangaren kasa da kasa, Archbishop Gabriele Giordano Caccia jakadan fadar Vatican a kasar Phlipine ya bayyana matukar jin dadinsa dangane da samun wata bababr kyauta daga Iran.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Archbishop Gabriele Giordano Caccia wanda shi ne jakadan fadar Vaticana  birnin manila na kasar Philipine, ya samu kyautar wani allo na tarihi da aka rubuta  aIran, wanda yake dauke da waya daga cikin littafin Linjila aya ta 21 a cikin Luqa.

A cikin abin da ya rubuta kan wannan lamari ya bayyana cewa:

Malama Qaqvi

Hakika na farin ciki maras misiltuwa kan samun wannan allo, wanda yake da matukar muhimmanci a wurina, musamman ganin matsayin allon da kuma ranar da aka bayar da shi kyauta a gare ni, wato ranar jamhuriyar muslucni ta Iran.

Abin tuni dais hi ne, wannan allo wanda aka rubuta shi dauke da ayar Linjila, wannan aya ta yi daidai da aya ta 6 da ke cikin kur'ani a cikin surat Inshirah (Hakika lallai tsanani yana tare da sauki).

3695479

 

 

 

 

 

 

 

captcha