Kamfanin dillancin labaran IQNA ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran Saudiyya cewa, ana shirin gudanar da taron cika shekaru hamsin da kafa kungiyar OIC a birnin Jiddah.
An kafa kungiyar ta hadin kan kasashen musulmi ne a shekara ta 1969 tare da halatar mambobi kasashe 57 a birnin Rabat na kasar Morocco.
A karon farko a 1970 an gudana da taron ministocin hakokin waje na kasashe mambobin kungiyar a birin Jiddah na Saudiyya.
Tun daga shekara ta 2016 Yusuf Usaimin ne babban sakataren kungiyar, wadda take ci gaba da gudanar da harkokinta da suka hada da zama na shekara-shekara na shugabannin kasashen musulmi.