Tashar alalam ta bayar da rahoton cewa, a karshen daren jiya Litinin 23 ga watan Maris, mutane da dama sun hau kan rufin gidajens a birnin Qods suna kabbarori, suna masu rokon Allah ya kawar da bala'in corona ga dukkanin al'ummar musulmi.
Domin kauce wa yaduwar cutar corona, a jiya an rufe masallacin aqsa baki daya, tare da dakatar da dukkanin ayyukan ibada acikinsa.