Bangaren yada labarai na cibiyar kusanto da mazhabobin muslucni ta duniya ya sanar da cewa, a jiya shugaban kasar Turkiya Rajab Tayyib Erdogan ya aike da sakon ta’aziyyar rasuwar Ayatollah Taskhiri shugaban kwamitin koli na cibiyar.
Darya Uras jakadan kasar Turkiya a birnin Tehran ya tuntubi shugaban cibiyar Hamid Shariyari, kuma ya isar masa da sakon shugaba Erdogan, inda ya nuna alhininsa matuka dangane da rasuwar wannan bababn malami, wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen hidima ga addini da kuma al’ummar msuulmi.
rasuwar