Shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa UAE, Khalifa Bin Zayed al- Nahyan ya soke dokar da ta hana yin alaka ta kasuwanci da tattalin arziki da haramtacciyar ƙasar Isra’ila a ci gaba da ɗaukar matakan ƙulla alaƙa tsakanin ƙasarsa da Haramtacciyar ƙasar Isra’ilan.
A yau Asabar ne Kamfanin dillancin labaran UAE ɗin ya bayar da labarin cewa a wata doka da ya fitar a yau ɗin nan Khalifa Bin Zayed Al Nahyan ya ba da umurnin soke dokar da ta hana mu’amala ta kasuwanci da Isra’ilan wanda a halin yanzu hakan zai ba da damar ƙulla alaƙoƙi na kasuwanci tsakanin UAE din da Isra’ila.
A ranar 13 ga watan Augustan nan ne dai shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa UAE da Isra’ila sun cimma yarjejeniyar ƙulla alaƙa a tsakaninsu a matakin farko na ci gaba da ƙoƙarin da ake yi na ganin sauran ƙasashen larabawa sun shigo sahu.
Wannan sanarwa dai ta fuskanci tofin Allah tsine daga ɓangarori daban-daban na duniyar larabawa da na musulmi.