Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Watan cewa, an gudanar da ayyukan share kura a dakin ka’aba a gaban yarima mai jiran gado na kasar Saudiyya a madadin sarkin wannan kasa da wasu yarima da manyan malamai da kuma jami’an haramin Makkah.
A cikin wannan aiki na shekara-shekara, wanda a al'adance ake daukarsa a matsayin wani bangare na al'adar kotunan Saudiyya, sarkin da kan sa yana goge da kakkabe kura a dakin Ka'aba.
Bayan shiga dakin ka'aba sarki yakan yi dawafi a dakin Allah sannan bayan ya yi sallar tawafi raka'a biyu sai ya shiga dakin ka'aba sannan bayan ya yi kura ya yi salla raka'a biyu. Ana wanke Kaaba da ruwan zamzam da ruwan fure.
Aikin na bana ya samu halartar Yariman Saudiyya mai jiran gado a madadin Sarkin kasar.