Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, an gudanar da taron debe kewa da kur’ani mai tsarki ne a ranar Talata 25 ga watan Yuni, kuma a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan Idin Ghadir Khum, tare da halartar shuwagabannin cibiyar kula da harkokin addini ta Hosseiniah Fatima Al-Zahra (AS). kuma a wani bangare, Seyyed Mohammad Hosseinipour, makarancin kasa da kasa na kasar Iran , ya karanta ayoyi daga kur’ani mai tsarki.
A cikin wannan taro, Hosseinipour ya karanta aya ta 1 zuwa ta 5 a cikin suratu Tahirim da aya ta 7 da ta 8 a cikin suratul Bayyinah .