IQNA

Martanin Netanyahu game da kisan Hassan Nasrallah

16:55 - September 29, 2024
Lambar Labari: 3491949
IQNA - A martaninsa na farko na rashin kunya game da kisan gillar da aka yi wa Sayyid Hasan HasNasrallah, firaministan gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra'ila ya bayyana cewa: Har yanzu ba a gama aikin Isra'ila ba, kuma za ta dauki karin matakai nan da kwanaki masu zuwa.

Tashar Aljazeera ta bayar da rahoton cewa, a cikin wani faifan bidiyo mai nuna rashin kunya ga shahadar Sayyid Hasan Nasrallah, wanda ya haifar da zanga-zangar manyan mutane da kungiyoyi daban-daban na kasa da kasa, ya yi da'awar cewa: Korar Nasrullah ya kasance wani sharadi da ya wajaba wajen sauya ma'auni a bangaren mulki a yankin.

Ya yi da'awar cewa: Yanzu muna fuskantar sauyin tarihi kuma kawar da Nasrallah wani muhimmin mataki ne na cimma wata manufa da aka kayyade, wato komawar mazauna arewa (yakunan da aka mamaye) gidajensu.

Da yake yin biris da irin gagarumar galaba da wannan gwamnatin ta yi a lokacin yakin Al-Aqsa, Netanyahu ya ci gaba da cewa: Mun samu gagarumar nasara; Amma aikin bai kare ba kuma za mu fuskanci kalubale a cikin kwanaki masu zuwa.

Idan dai ba a manta ba a yammacin ranar Juma’a ne kuma a daidai lokacin da Netanyahu yake birnin New York, sojojin gwamnatin sahyoniyawan sun kai munanan hare-hare a yankunan kudancin birnin Beirut, inda Sayyid Hassan Nasrallah babban sakataren kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya yi shahada. .

Har ila yau, wannan harin ya kai ga shahada da raunata wasu jami'ai da 'yan kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon da daruruwan mutane da suka hada da mata da kananan yara da dama.

 

 

4239399

 

 

captcha