Bangaren Tunani da Fikira na cibiyar koyar da Alkur'ani a Iran Iqna ne ya yi wata tattaunawa ta musamman da malummai masana masu bincike kan fassirin Amirul mu'umina (AS) suna ta kokarin danganta hadisan Imam Ali (AS) da maganganunsa da ayoyin Alkur'ani da ganin duk wani abu da yake bayyanawa ya yi dai da ayoyin Alkur'ani kuma musamman litafinsa na Hasken nahajul Balaga .A cikin wannan litafi idan muka yi dubi a cikin wasikar day a rubutawa dansa Imam Hasan (AS) za mu fahimci irin nasiha da tarbiya irin ta Alkur'ani da wannan wasika ta kumsa bugu da kari za mu fahimci matsayi da dokakar wannan bawon Allah wanda ya nuna kauna da soyayya ga yayansa da hakan bai hana shi tarbiyartar da su tarbiya ta gari madaidaiciya cikin tafarkin Allah madaukakin sarki.
363773