IQNA

Haramtacciyar kasar Isra'ila ta rushe cibiyoyin ilimi na Palastinawa.

10:48 - February 17, 2009
Lambar Labari: 1744833
Bangaren kasa da kasa: A hare-haren ta'addancin da Haramtacciyar kasar Isra'ila ta kai kan Gaza tsawon kawanaki 22, ta rushe cibiyoyin ilimi da al'adu na palastinawa da ke cikin yankunan Zirin Gaza.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga shafin internet na (Alarab online) cewa; mataimakin shugaban kungiyar lauyoyi larabawa Abdulazim Almagribi ya fadi yau a wajen taron birnin Ribat, da ke tattauna ayyuakan kisan kiyashi da yahudawan sahyuniya suka yi kan al'ummar Gaza, cewa a hare-haren da sojin yahudawan sahyuniyan suka kai kan Gaza na tsawon kwanaki 22, sun rushed a dama daga cikin cibiyoyin ilimi da al'adu, da suka hada da makarantu da jami'oi, wanda hakan ya cancanci a gurfanar da shugabannin gwamnatin yahudawan a gaban kotun manyan laifuka ta duniya domin fuskantar shari'a.

364631
captcha