Bangaren kasa da kasa: wata tawagar masu jinkan dan adam daga birnin London na kasar Birtaniya, ta kama hanyar zirin Gaza, domin kai dauki ga al'ummar yankin.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga kafar yada labarai ta BBC cewa; tawagar masu gudanar ayyukan jin kai ta London ta kama hanyar Gaza, domin kai taimako na kayayyaki da aka kaddara kudinsu da Pound miliyan daya. Daga cikin kayayyakin kuwa hard a motoci 100, da suka hada da na kashe gobara, da na daukar marassa lafiya, da kuma motocin daukar kaya, a cikin kayan kuma akwai kayan abinci, da magunguna, tufafi, barguna,da dai sauransu.
George Galawi wani dan majalisa ne a kasar Birtaniya, wanda ya yaba da kokarin da masu bayar da agajin suka yi, inda ya bayyana cewa; taimakon al'ummar gaza taimako ne ga 'yan adamtaka.
364544