IQNA

Amurka Na Kokarin Dawo da Mutuncinta Da Ya Zube A Wajen Musulmi

17:56 - February 19, 2009
Lambar Labari: 1746086
Bangaren kasa da kasa: Sakatariyar harkokin wajen kasar Amurka Helary Clinton ta bayyana cewa; gwamnatin Obama na da zimmar ganin ta kyautata dangantakarta da kasashen musulmi tare da yin aiki da su kafada da kafada.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga jaridar (Washington Post) cewa; a lokacin da take gabatar da wata lacca a jami'ar Tokyo a kasar Japan a ranar Talatar da ta gabata, Helary Clinton ta bayyana cewa Amurka za ta ci gaba kokarin kyautata danganatakarta da kasashen musulmi, domin kawo karshen rashin fahimtar juna da ke akwai tsakanin duniyar musulmi da Amurka. Ta kara da cewa; a matsayinta na kirista ta san cewa akwai kiristocin da aka tafka tabargaza da sunan addini, amma hakan ba yana wakiltar addinin kiristanci ba ne, haka nan ma musulmin da suke aikata ayyukan wuce goda da iri da sunan addinin musulunci ta san ba suna wakiltar addini musulunci ba ne.

365864

captcha