Bangaren Ziyasa Da Zamantakewa: Cibiyar da ke kula da waqf da sauran ayyukan alhairi a garin Khomen da ke cikin Lardin Isfahan, ta bayyana waqf a matsayin daya daga cikin abubuwan da ke ciyara da rayuwar dan adam a gaba.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya habarta cewa; shugaban reshen cibiyar da ke kula waqf da ayyukan alhairi a garin Khomen da ke cikin lardin Isfahan (Ali Emami) ya bayyana cewa; shi waqf wato ( kebance wani abu domin amfanin jama'a saboda Allah) wata kyakkaywar sunna ce a cikin addinin musulunci, wadda ta taimaka wajen raya addini da rayuwar al'ummar musulmi.
Ya ce masu bayar da waqf sun taka rawa wajen taimaka ma harkokin kiwon lafiya, gina cibiyoyin addini da dai sauransu.
369422