Bangaren Siyasa: Bangaren sojin sa kai na jami'ar Imam Sadiq (AS) da ke birnin sun bukaci ministan shari'a na kasar Iran, da ya taka rawa wajen ganin a sake raya kudirin Majalisar Dinkin Duniya na shekarar1970 da ya haramta duk wani aikin nuna wariya.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga bangaren dalibai sojin sa kai na (Basij) na jami'ar Imam Sadiq (AS) cewa; daliban sun rubuta wata wasika zuwa ga ministan shari'a na kasar Iran, da a cikin suka kirayi ministan da ya taka rawa wajen ganin an sake farfado da kurin Majalisar Dinkin Duniya mai lamba 3379, da aka fitar a ranar 10 ga watan Nuwamban 1970 wanda ya bayyana ayyukan Haramtacciyar Kasar Isra'ila a kan al'ummar Palastinu a matsayin ayyuka na nuna wariya, amma sakamakon goyon bayan da Amurka take baiwa gwamnatin yahudawan sahyuniya aka manta wannan kudiri.
A bangare guda kuma sun bukaci da gyrfanar da gwamnatin yahudawan sakamakon ayyukan yaki da ta aikata na tsawon kwanaki 22 a kan al'ummar Gaza marassa kariya.
370875