Cibiyar kula da harkokin alkur'ani a Iran Ikna ce bayan ta nakalto daga majiyar labarai ta Masar Sana ta watsa rahoton cewa: mahalarta taron na gurin Shakatawa na Sharmun Sheikh a cikin bayanin bayan taro sun jaddada wajibcin gwamnatin HKI ta bude mashigar Rafah kuma dole ta kiyaye dokokin kasa da kasa da ta canja matakin kai wad a lalata guraren kasuwanci da na fararen hula. A wani bangare na bayanin bayan taron kasa da kasa kan sake gin aGaza sun bukaci HKi da ta ba su damar isar da abubuwa na farko da ake bukata kafin fara sake gina gurare da gidajen da ta ruguza. A wannan taron kimanin dala biliyan hudu da miliyon dari hudu da tamanin aka yi alkawalin bayarwa.
372164