IQNA

Sarkin Jodan Ya Jaddada Kafa Gwamnatin Palasdinu Mai Cin gashin kanta

14:05 - March 04, 2009
Lambar Labari: 1751728
Bangaren siyasa da zamantakewa: tattaunawa tsakanin kungiyoyin Palasdinu da kuma tsakaninsu da HKi ya kasance ya taimaka wajen wajabta kafa gwamnatin Palasdinu mai yanci in ji Sarkin Jodan Malik Abdalla na biyu.
Cibiyar da ke kula da harkokin alkur'ani a Iran Ikna ce daga Jodan ta watsa rahoton cewa: malki Abdalla na biyu na Jodan ya fitar da wani bayani da a cikinsa yake jaddada wajibcin kafa gwamnatin Palasdinu mai cin gashin kanta .Kuma ya kara da cewa ana jin haka ta samu ta hanyar tattaunawa tsakanin Palasdinawa da kuma gwamnatin Palasdinu a dabra daya kuma hanyar tattaunawa ita ce za ta kawo karshen rikici a palasdinu.malik abdallah ya fadi haka ne a lokacin da yake ganawa da Jorge Mishel manzon musamman na shugaban kasar Amerika Barak Obama a yankin gabas ta tsakiya a kokarinsa na ganin sun kawo karshen rikici a yankin.

371367

captcha