IQNA

Malaman Masar Ba Su Amince Da Canja Littafan Darasi Na Musulmi Ba

16:27 - March 05, 2009
Lambar Labari: 1752091
Bangaren kasa da kasa: Tun bayan da jami'ar Al-azhar tare da fadara Vatican suka aamince da kawo canji a cikin littafan darasi na musulmi kirista, kan bangarorin da ke sukar wasu addinai, malaman Masar Suka nuna rashin amincewarsu da hakan.
Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga shafin internet na (Islam online) cewa; malaman kasar Masar sun fitar da wani bayani da a cikinsa suka bayyana rashin amincewarsu da duk wani batun cire wasu daruusa da ke sukar wasu addinai, bayanin ya ce littafan musulmi ba su bukatar a cire wani abu daga cikinsu, domin babu sukar wasa addinai ko mabiyansu a cikin littafan musulmi. Bayanin ya ce littafan da ake koyar da su a makarantun kasashen turai dai su n eke bukatar kwakwarima, domin kuwa su ne suke sukar addinin musulunci da mabiyansa.
A zaman da wakilan jami'ar Azhar da na fadar Vatican suka gudanar a kwanakin baya ne suka amince kan cewa a cire duk wasu darussa da suke sukar addinai a cikin littafan darasi na kasashen musulmi da kirista.

372825
captcha