Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga kamfanin dillancin labaran SANA cewa; Sakatare janar na majalisar dinkin duniya Ban Ki-Moon ya nuna matukar damuwa dangane da halin da al'ummar Gaza ke ciki, inda ya kirayi Isra'ila da ta gaggauta janye killacewar da take yi wa yanzkin Zirin Gaza ba tare da wani bata lokaci ba. A cikin wata wasika da ya aike wa masu taron birnin Alkahira, ya bayyana cewa ya zama wajibi a cimma matsaya kan makomar Gaza, domin kuwa al'ummar yankin suna cikin wani mawuyacin hali, kuma ya zama wajibi a cimma matsaya dangane da batun bude wuta, kuma kirayi Isra'ila da ta janye killacewar da take yi wa yankin Gaza cikin gaggawa, domin a cewarsa hakan na ci gaba da jefa al'ummar yankin cikin mawuyacin hali na rayuwa.
377398