Kamfanin dillancin labaran Ikna ya zanta da daya daga cikin masu gudanar da shirye-shiryen sinima da suka yi fice a kasar Iran (Abdulriza Akbar) inda ya bayyana cewa; shirin sinima da ake gudanarwa a Iran zai iya taka gagarumar rawa wajen isar da sakon kur’ani tare da wayar da kan al’umma kamar yadda ya kamata, ya ce masu gudanar da shirye-shiryen sinima da sauran ayyukan al’adu a Iran, suna taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan al’umma dangane da abubuwa da dama da suka shafi rayuwar jama’a ta zamantakewa a addinance, kuma za su iya taka rawa kamar yadda kamata wajen isar da sakon kur’ani a cikin shirye-shiryensu na sinima da suke gudanarwa.
379020