Kamfanin dillancin labaran Ikna ya nakalto daga cibiyar kula da yada ilimi da al'adun Musulunci ta ISESCO cewa; kungiyar jami'o'in kasashen musulmi ta sanar cewa za ta halarci taron jami'o'i na duniya da za a gudanar a kasar Mexico a cikin makon nan. Wannan dai shi ne karo na uku da kungiyar hadin kan jami'oi ta duniya AIU za ta gudanar da babban taronta, inda za a tattauna muhimman batutuwa da suka shafi harkokin ilimin jami'a a matsayi na kasashe da kuma matsayi na duniya. Jami'oin kasashen musulmi za su halarci zaman taron ne domin gabatar da mahangarsu kan lamurran da suka shafi al'adu da ilimi, domin samun karfafa junatsakaninsu da sauran jami'oi na duniya.
389933