IQNA

Gart Wildars Ya sake Kaddamar Da Fim Din Fitina Ta Biyu

15:50 - April 20, 2009
Lambar Labari: 1766530
Bangaren Kasa da kasa; Mai tsautsaran ra'ayin nan dan kasar Holand Gart Wildars ya sake yin wata fim ta Fitina ta biyu da ke cin mutuncin musulunci .
Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran Ikna ce ta jiyo daga jaridar Aliktisadiya al-elaktroniya ta kasar Saudiya cewa: Gart Wildars dan dan majalisa mai tsananin gaba da addinin musulunci ya sake kaddamar da wata fim ta fitini ta biyu da a ciki yake cin mutuncin addinin musulunci kuma duk da cewa an yi ta yi masa kashedin kar ya kuskura ya kaddamar da wannan fim din amma ya yi kunnan uwar shegu da shure duk wani kira da musulmi suka yi masa kan wannan mummunan mataki na san a batanci kan addinin musulunci da kuma takwalar fada a fili.

389535

captcha