Cibiyar da ke kula da harkokin kur'ani a Iran ce ta watsa rahoton cewa: Muhammad husein Saffar Hurandi ministan al'adu da Irsahdi na jamhuriyar musulunci ta Iran a karshen zaman da ministocin al'adu na kasashe da suke mambobi a hukumar lura da dangantaka ta al'adu a lokacin ziyara da ganawarsa da Alaksandre Udiyuf ministan al'adu na kasar rasha ya yi bayanin cewa: bawa al'adu muhimanci yana daga cikin dalilan cimma nasara a harkokin Sinema a Iran da kuma Rasha tare da bukatar kara inganta dangantakar kasashen biyu da al'ummominsu ta fuskoki daban-daban da suka hada da rubuce-rubuce da binciken kan al'adun kasashen biyu.
396829